Monday, March 14, 2016

Jos: Matasa na zanga-zanga saboda kashe yan uwan su 4

– Zanga-zanga ta barke a garin Jos da safiyar ranar Litinin


– Wannan ya faru ne saboda ana zargin yan banga da kashe matasa 4


– An kona Police station


Garin Jos

Rikicin a unguwar Rukuba, Jos



Zanga-zanga ta barke a garin Anguwar Rukuna da safiyar Litinin 14 ga watan Maris. Wannan ya faru ne saboda zargin da ake yima wasu yan banga da kashe mutane 4 a unguwar wadanda basu da laifin komai.


Wata majiya ta bayyana cewa matasa 4 an kashe su ne da daren Lahadi, 13 ga watan Maris. Jaridar Breaking Times ta bayyana cewa wasu matasa da suka fusata sun kona wata police station dake a unguwar domin nuna rashin amincewar su da abunda yan bangar suka aikata a jiyan.


A cikin garin Jos

Wata wuta mai ci. Jos



 


Garin Jos

Wasu matasa a Rukuba, Jos



Wannan dai yana daya daga cikin rikicin da garin ya fuskanta tun shigar sabuwar shekara ta 2016.


KU KARANTA: Yan fashi sun farma yar jarida


A shekarun baya Jihar taga rigingimu daya inda ake rikici tsakanin yan asalin jihar da kuma mazauna. Anyi wasu kazamun rigingimu a 2005, wanda ya sanya tsohon shugaban kasa Obasanjo ya cire gwamna Dariye a lokacin.


Haka kuma anyi rikici a 2009 a lokacin mulki mariganyi tsohon shugaban Kasa Ummaru Musa Yar’adua. Jihar  ta dade a karkashin dokar ta baci saboda irin rikice-rikicen da ake yi.


The post Jos: Matasa na zanga-zanga saboda kashe yan uwan su 4 appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.







Jos: Matasa na zanga-zanga saboda kashe yan uwan su 4
Previous Post
Next Post

About Author

0 Comments: